Rundunar Sojin Najeriya ta musanta rahotannin da ke yawo a wasu kafafen sada zumunta da ke cewa an yi yunƙurin juyin mulki a ƙasar.
A jawabin da Kakakin Rundunar, Brigedi Janar Onyema Nwachukwu, ya bayar, ya bayyana cewa labaran da ake yadawa babu tushe kuma suna da nufin tada hankalin jama’a. Brigedi Nwachukwu ya ce.
> “Babu wani yunƙuri na juyin mulki da ya faru a Najeriya. Duk wani labarin da ya fita a kafafen sada zumunta game da hakan, ba gaskiya bane.”
Haka kuma, Rundunar ta yi kira ga ‘yan Najeriya da su kasance masu lura da irin labaran da suke karantawa da raba wa wasu, tare da tabbatar da sahihancin bayanai daga majiyoyi na gaskiya kafin su yada su.
Masu sharhi a kan wannan batu sun bayyana cewa irin wannan yaduwar labaran karya na iya haifar da tashin hankali da rudani a tsakanin al’umma. Don haka, Rundunar Soji ta jaddada muhimmancin riko da gaskiya da natsuwa a yayin karanta ko rabawa labarai.

Comments
Post a Comment