A ranar 18 ga Oktoba, 2025, Hukumar Tace Finafinai da Ɗab’i ta Jihar Kano ta kama Faruk Abubakar bisa zargin wallafa hotuna da rubuce-rubucen batsa a shafinsa na sada zumunta. Rahotanni sun tabbatar da cewa an kama shi ne a ofishin 'yan sanda na Bompai, Kano, bisa umarnin hukumar karkashin jagorancin Abba Mustapha Inuwa.
Bashir Musa Jammaje, wani abokin Faruk, ya tabbatar da sahihancin labarin bayan ya tuntubi Faruk da kansa, sannan daga bisani ya kira shugaban hukumar, Abba Mustapha, wanda ya tabbatar masa da cewa lamarin gaskiya ne. Ya kuma bayyana cewa hukumar ta jima tana kiran Faruk saboda irin wallafe-wallafen batsa da yake yi a shafukansa na sada zumunta, amma ya kasa amsa kiran da suke yi masa. Saboda haka, hukumar ta ɗauki matakin haɗa hannu da jami’an tsaro don kamo shi domin ya amsa tambayoyi.
Bashir ya roƙi hukumar da ta yi sassauci a kan Faruk, yana mai tabbatar da cewa za a duba lamarin cikin adalci. Ya kuma yi kira ga masu amfani da kafafen sada zumunta, musamman a Kano, da su guji wallafa abubuwan da suka sabawa tarbiyya da dokokin jihar, tare da mutunta hukumomin gwamnati.

Comments
Post a Comment